KatsinaTimes
Mazauna ƙauyukan Kungaboku da Paze da ke Babban Birnin Tarayya Abuja sun fara barin gidajensu sakamakon wata wasiƙar barazana da ake zargin ‘yan bindiga ne suka rubuta, wadda ke nuna shirin kai hare-hare a yankunan.
Rahotanni sun bayyana cewa an gano wasiƙar ne a cikin jakar makaranta ta wani ɗalibi a wata makaranta mai zaman kanta da ke Paze. A cikin wasiƙar, waɗanda ake zargin ‘yan bindiga ne suka yi barazanar kai hare-hare kan ƙauyukan Kungaboku da Paze domin ɗaukar fansar kashe wani kwamandansu.
A ranar 7 ga watan Maris, sojojin Bataliya ta 7 ta Guards Brigade ta rundunar Nigerian Army tare da haɗin gwiwar jami’an 'yansanda Nigeria Police Force da kuma ‘yan sa-kai suka ceto mutane 19 da aka sace a yankin.
An gudanar da aikin ceton ne a yankin Gidan Dogo da ke ƙaramar hukumar Bwari Area Council. A yayin farmakin, rahotanni sun ce an kashe wani ɗan bindiga yayin da sauran suka tsere da raunukan harbin bindiga.
Har ila yau, jami’an tsaro sun kwato bindiga kirar AK-47 guda ɗaya da kuma wata bindiga da aka ƙera a gida daga wurin.
Yadda Aka Gano Wasiƙar Barazanar
Wata malama ce ta gano wasiƙar barazanar a cikin littafin ɗalibi yayin da take duba aikin gida a makarantar. Bayan sanar da jami’an tsaro, an gayyaci ɗalibin, iyayensa, malamar da kuma shugabannin makarantar domin yi musu tambayoyi kafin daga bisani a sake su.
Lamarin ya bazu cikin sauri a tsakanin mazauna yankin ta hanyar ƙungiyoyin al’umma da kuma kafafen sada zumunta, abin da ya ƙara jefa mutane cikin fargaba.
Kafin bayyanar wasiƙar ma, ana zargin ‘yan bindiga sun kai hari a wani matsugunin Fulani da ke Kungaboku inda suka sace mata uku tare da neman kudin fansa na naira miliyan 70.
Rahoton News Agency of Nigeria (NAN) ya nuna cewa Kungaboku da Paze, da ke kusa da Byazhin a yankin Kubwa cikin Bwari Area Council, sun fuskanci hare-hare da dama a ‘yan watannin nan.
A watan Oktoban 2025, an kashe wani likitan dabbobi, Ifeanyi Ogbu, a Kungaboku bayan an sace shi tare da ‘ya’yansa uku.
Hakazalika, a ranar 5 ga Maris, ‘yan bindiga sun kai hari a Kungaboku inda suka sace wani tsohon jami’in soja, Bankole Ganiyu, tare da yara uku. Matarsa wadda jami’ar ‘yan sanda ce da wasu yara biyu sun samu tserewa daga harin.
A wani hari a wannan rana, maharan sun kashe wani ɗan sa-kai da ke bakin aiki tare da sace ma’aikata uku a wani matsugunin manoma.
Sakamakon sabuwar barazanar, jami’in ‘yan sanda mai kula da yankin Byazhin ya kira wani taron gaggawa a ranar Asabar a fadar shugaban al’ummar Kungaboku, Chief Ishaya Jagaba.
A taron, ‘yan sanda sun tabbatar da wanzuwar wasiƙar barazanar amma sun tabbatar wa mazauna yankin cewa ana ɗaukar matakan tsaro domin hana kai harin.
An shawarci mazauna yankin da su kasance cikin shiri tare da kula da ayyukan masu hayar babura da masu tara shara, waɗanda a wasu lokuta ake zargin suna ba maharan bayanai.
Haka kuma an buƙaci al’umma su riƙa tantance bakin da ke shigowa yankin domin tabbatar da cewa ba masu laifi ba ne.
Jami’an tsaro sun kuma yi alkawarin gudanar da sintiri na dare da rana a yankin domin dakile duk wani yunkurin kai hari.
Duk da haka, fargaba na ci gaba da mamaye mazauna Kungaboku da Paze, inda wasu gidaje suka riga suka zama babu kowa yayin da mutane ke jiran ganin ko matakan tsaron da aka yi alkawari za su hana sabon hari.